Yan tawaye a arewacin Chadi da sojojin ƙasar suka zarga da kashe shugaba Idris Deby sun ce a shirye su tsagaita wuta da kuma tattauna batun sasantawa a siyasance, a cewar kakakin ƴan tawayen a ranar Lahadi.
Ƴan tawayen FACT a Chadi da ke arewacin Chadi kan iyaka da Libya a ranar 11 ga Afrilu suka tunkari N'Djamena, suna kiran kawo ƙarshen mulkin Idriss Deby na shekaru 30.
Sun kusan shiga N'Djamena, kusan tazarar kilomita 200 zuwa 300 kafin sojoji suka kore su.
An kashe Idriss Deby a ranar Litinin yayin da ya kai wa sojojin Chadi ziyara a fagen daga.
Mutuwarsa ta girgiza ƙasashen Tsakiyar Afrika da yankin Tafkin Chadi da Sahel saboda rawar da yake takawa ga yaƙi da ƴan bindiga.
Kakakin FACT Kingabe Ogouzeimi de Tapol ya shaida wa Kamfanin dillacin labarai na Reuters cewa a shirye suke su tsagaita buɗa wuta da kuma tattaunar da ta mutunta ƴancin Chadi ba juyin mulki ba.
Bayan mutuwar Deby, Sojojin Chadi suka kwaci mulki inda suka ɗora ɗansa Mahamat Idriss
Deby tare da alƙawalin zai yi riƙon ƙwarya na watanni 18 kafin gudanar da zaɓe. Matakin da ƴan adawa da ƴan tawaye suka kira juyin mulki
Rahotun BBC Hausa.
https://chat.whatsapp.com/IM8Uuxtia6qBsdKcEszx7s
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari