Idan ka gina mace tamkar ka gina al'umma ne - Gwamna Bagudu


Gwamnan jihar Kebbi Abubakar Atiku Bagudu ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da taimakawa mata domin idan ka gina mata tamkar ka gina al'umma ne maki daya.

Bagudu ya fadi hakan ne cikin wata sanarwa da mataimakinsa na musamman kan harkokin yada labarai Yahaya Sarki ya fitar, yana ruwaito cewa Bagudu ya ce "Yawan taimakon da za mu iya bai wa mata yanayin yadda al'umarmu za ta habaka".

Bagudu ya bayyana mata a matsayin wadanda duk wahalar da aka sha ta annobar korona ta matsin tattalin arziki ta kare a kansu.

Gwamnan ya bayyana haka ne a wajen wata makala da jihar ta shirya wa mata domin zuwan watan Ramadana, wadda aka yi wa taken "Muhimmiyar rawar da mata za su iya taka wa a Musulunci."

Makalar da aka yi ta mayar da hankali ne kan yadda mata za su tafiyar da gida a lokacin annobar korona, wajibin da ke kan mata na kula da iyali a yayin matsin tattalin arziki da kuma yadda za a kawo karshen cin zarafin mata.

Rahotun BBC Hausa


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/Cw2uhGNZiIzGM88PV4gpOI

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN