Shanu 50 Sun Sake Yin Mutuwar Ban Mamaki a Wani Gari a Ondo


A kalla shanu 50 ne suka mutu a wani yanayi mai daure kai a Akungba-Akoko, a karamar hukumar Akoko na jihar Ondo, Vanguard ta ruwaito.

Kazalika Jarida legit ta ruwaito cewa an gano cewa lamarin ya faru ne a ranar Litinin da yamma a yankin Ibaka na garin.

Wani mazaunin Akungba, Oshk Fela Castro ya shaidawa SaharaReporters cewa shanun sun mutu ne bayan cin wani abu da ake zargin guba ne.

Ya shawarci mazauna garin su guji sayar nama mai araha domin yana zargin wasu masu sayar da nama marasa gaskiya za su iya sayar da naman shanun da suka mutu.

"Bayanin da na samu shine shanun sun mutu bayan cin wani abu da ake zargin guba ne. Kuma an fada min cewa duk wanda ya ci naman zai iya mutuwa saboda gubar. Shanun sun fara rubewa bayan minti 30 bayan mai su ya gano sun ci guba.

"Don Allah ku fadawa makwabta da abokanku su yi takatsantsan wurin siyan nama. Ina son jami'an tsaro su tabbatar ba a siyar da naman wadannan shanun da suka mutu ba," in ji shi.

A 2019, an ruwaito cewa tsawa ta kashe kimanin shanu 36 a Ijare, karamar hukumar Ifedore a jihar Ondo.

Duk da ikirarin da wasu mazauna garin suka yi na cewa tsafi ne ya kashe shanun saboda Fulani sun keta cikin wurin bautar masu addinin gargajiya, yan sanda sun ce tsawa ce kawai.


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/Cw2uhGNZiIzGM88PV4gpOI

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN