Yan bindiga cikin duhun dare ranar Lahadi, sun farmaki kauyen Mussuru da ke Mazabar Dan Umaru a karamar hukumar Danko-Wasagu da ke Masarautar Zuru a kudancin jihar Kebbi.
Yan bindigan sun shiga kauyen ne da misalin karfe daya na dare ranar Lahadi suka dinga barin wuta da bindiga, daga bisani suka dauke wata matar aure yar shekara 35 mai suna Mairi Alhaji Isiya.
Kawo yanzu dai babu Karin bayani kan irin barnar da harin na ranar Lahadi ya haifar. Sai dai mun samo cewa har yanzu Yan bindigan basu tuntubi iyalin matar da suka dauke ba.
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/HUEzyk9QvHZ6kSk4bH2U6K
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari