Rundunar yan sanda ta kama masunta yan kabilar jukun su uku kan zargin hannu cikin harin da aka kai wa tawagar Gwamna Samuel Ortom na jihar Benue a hanyar Tyo Mu a Makurdi, The Nation ruwaito.
Jaridar legit ta ruwaito cewa mai bawa gwamnan shawara kan tsaro, Kwanel Paul Hemba, ya tabbatar da hakan yayin da ya ke zagayawa da manema labarai wurin da aka kai harin a ranar Talata.
Hemba ya ce yan sandan sun ga masuntar kusa da wurin da aka kai harin kuma ana bincike a kansu.
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/Cw2uhGNZiIzGM88PV4gpOI
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari