Shugaban kungiyar Lauyoyi na jihar Kebbi Barista Kabiru Aliyu ya tabbatar da tsunduma da ilahirin Lauyoyi karkashin kungiyar Lauyoyi na jihar Kebbi sun fara kaurace wa Kotuna a fadin jihar daga ranar 3 ga wata Fabrairu har tsawon mako uku.
Barista Kabiru Aliyu ya jaddada haka a wani faifen bidiyo da kungiyar Lauyoyi na jihar Kebbi ta sanar wa gudan Talabijin na kasa watau Nigeria Television Authority NTA ranar Talata a garin Birnin kebbi.
Barista Kabiru ya ce "Abubuwa da dama sun faru a kasar Zuru dangane da tsaro wanda mun yi kira ga Gwamnatin jiha da Masarautar Zuru su dauki maki kan kashe kashe da yan sa kai ke yi
Ya ce "Sun dauki alkawari a fadar Mai Martaba Sarkin Zuru cewa ba za su sake sa hannu a harka da ta shafi shari'a ba. Sai ga shi daya daga cikin manya manyan Lauyoyi wanda muke da, wanda sun yi karatu tare da Chif Justis na Najeriya, sun dauke shi sun bashi kashi a kan wata shari'a da yake tsaya ma wani a Kotu, sun ce idan bai fitar da hannun shi ba a shari'ar za su kashe shi".
Ya kara da cewa "Ganin cewa akwai tsoratarwa da damuwa ga mu masu harkar shari'a bai kamata mu yi kasa a gwuiwa ba saboda kada wani abu a sake faruwa".
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/LKeYYgwzLbW8DdHbjNuEos
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari