Jaridar legit ta wallafa cewa Gwamnatin tarayya ta daga wa yan Najeriya da dama kafa kan shirin haɗa lambar NIN da layin waya wanda ke gudana a kasar.
Duba ga matsalolin da ake ta fuskanta, gwamnati ta kara wa'adin shirin har zuwa makonni takwas masu zuwa nan gaba.
Jaridar Punch ta ruwaito cewa daraktan harkokin labarai na hukumar sadarwa ta Najeriya, Ikechukwu Adinde ne yayi sanarwar.
Adinde ya ce ministan sadarwa, Isa Pantami ya isar da sakon a lokacin wata ganawa da kwamitin ministan kan rijistan NIN da Sim wanda ya gudana a ranar 1 ga watan Fabrairu, 2021.
Da wannan, sabon wa'adin rufe layukan a yanzu shine ranar 6 ga watan Afrilu 2021.
https://chat.whatsapp.com/LKeYYgwzLbW8DdHbjNuEos
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari