Yansanda sun yi wa Lauya kamun dan iska sakamakon yi wa yarinya fyade da cikin shege



Rundunar yansandan jihar Oyo ta kama wani mutum mai shekara 56 a Duniya Remi Oladiti, wanda ya ce shi Lauya ne, bisa zargin bugar da yarinya mai shekara 14 da haihuwa da kayan maye, tare da yi mata fyade sakamakon haka ta dauki cikin na gaba da Fatiha a unguwar Bodaji da ke birnin Ibadan.

Kwamishinan yansandan jihar Oyo Mrs Ngozi Onadeko, ta shaida wa manema labarai cewa ranar Alhamis da ta gabata iyayen yarinyar sun aike ta domin ta sayo Akamu. Amma sai Oladiti ya biyo ta ya dinga lallashinta har ya bata lemun kwalba ta sha, daga bisani sai ta dinga jin barci, bayan ta farka daga barci ne kawai sai ta gan kanta kwance tsirara a kan gadon Oladiti jini yana fitowa daga alaurarta.

Binciken Asibiti ya nuna yarinyar tana dauke da juna biyu na tsawon makonni 29.

Yansanda na ci gaba da bincike, yayin da aka tsare wanda ake zargi, wanda ya gaya wa yansanda cewa shi Lauya ne.


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/HUEzyk9QvHZ6kSk4bH2U6K

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN