Wata Lauya mai juna biyu ta gamu da ajalinta a hannun yan iska, duba abinda ya faru


Wata Lauya wacce ke dauke da juna biyu mai suna Nkiru Agbasu ta mutu bayan wasu matasa da ake zargin yan fashi da makami ne sun bude wuta kan motar da Nkiru ke ciki a kan tagwayen hanyar Warri zuwa Sapele a jihar Delta.

Shafin ISYAKU COM ya samo cewa Nkiru ce kawai ta mutu a cikin motar ta fasinja, bayan yan fashi dauke da bindigogi sun buda wa motar haya wuta yayin da motar ke kan hanyarta ta komawa Warri daga garin Sapele.

Emmanuel O. Uti, shugaban kungiyar Lauyoyi reshen Warri, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Yace " Tabbas lamarin ya faru. Fashi da makami aka yi wanda ya rutsa da ita bayan yan fashin sun harbi motar haya da take ciki. Ita kadai ce harsashi ya sameta kuma ta mutu.

Mun Sami labarin faruwar lamarin ne da karfe 5 na yamma, wata kila abin ya faru ne tsakanin rana zuwa yamma".


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/HUEzyk9QvHZ6kSk4bH2U6K

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN