Wani dan jaridar Muryar Amurka (VOA Hausa) dake dauko rahoto daga jihar Adamawa da Taraba, Ibrahim Abdulaziz ya mutu mumunan hadarin motar da ya auku a hanyar Gombe-Alkaleri Jaridar legit ta ruwaito.
Dan jaridar wanda yayi shekara 48 a duniya ya yi aiki da gidajen jaridu da yawa kuma ya yi shirye-shirye a gidajen rediyo irinsu Radio Gotel da FRCN Fombina FM Yola.
Iyalan mamacin sun tabbatar da labarin mutuwarsa, inda suka ce su biyu suka mutu a hadari.
Ya rasu yana da mata uku da yara tara.
Sakataren kungiyar yan jaridan Najeriya, shiyar jihar Adamawa, Fidelis Jocthan; ya yi alhinin rasuwar Ibrahim kuma ya yi addu'an Allah ya jikansa.
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/LKeYYgwzLbW8DdHbjNuEos
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari