Tambuwal ya fallasa yadda yan bindiga ke samun miyagun kwayoyi a Sokoto


Gwamna Aminu Waziri Tambuwal, ya yi zargin cewa mata masu tallar Fura da Nono na yi wa ’yan bindiga da sauran ’yan ta’adda a Jihar Sakkwato safarar miyagun kwayoyi Jaridar Aminiya ta wallafa.

Gwamnan ya yi furucin haka ne ranar Asabar yayin da fitaccen malamin addinin Islama, Sheikh Ahmed Gumi ya jagoranci shirin karbar tuban ’yan bindiga da aka yi wa lakabi GULBAR a birnin Shehu.

 “Wani takawarana, wani gwamna mai ci ya taba bani labarin wani abun da ya faru. Ya gaya mani cewa ta taba ziyartar wani kauye yana son sayen nono a wurin matan kauyen da suke fita cin kasuwar sayar da fura da nono.”

Lokacin da ya kira su, sai daya daga cikinsu ta tsere. Ya tambayi mene ne yake faruwa sai aka fada masa cewa ai ba tallar nono ta dauko ba face miyagun kwayoyi ne a cikin kwaryarta.”

“Ya gaya mani cewa yawanci ’yan bindiga da masu satar mutane da sauran ’yan ta’adda suna samun miyagun kwayoyi ne ta wannan hanya.”

“A saboda wannan dalili, dole ne mu tashi tsaye domin shawo kan wannan matsalar ta sha da fataucin miyagun kwayoyi, don idan ba haka ba za mu karasa kashe macijin ne ba tare da sare kansa ba,” in ji Gwamnan.

A cewarsa, “ya kamata mu lura da irin rawar da miyagun kwayoyi ke takawa wajen rura wutar ta’addanci da sauran munanan halaye.”


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/HUEzyk9QvHZ6kSk4bH2U6K

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN