Rahotanni daga Masarautar Zuru da ke kudancin jihar Kebbi sun ce Yan bindiga sun kai farmaki a kauyukan Ganyale da Doka da ke karkashin garin Unashi a karamar hukumar Danko/Wasagu da yammacin ranar Litinin 22/02/2021.
Yan bindigan sun yi awon gaba da shanaye, bayan sun halaka mutane tare da raunata wasu .
Sai dai mun samo cewa soji tare da taimakon Yan sa Kai, sun fuskanci Yan bindigan a yankin kauyukan Yababa, Cedkkubu da Doka.
Wannan harin na Litinin yana zuwa ne bayan harin Yan bindiga da ya yi sanadin kashe mutum 2, tare da sace mutane 9 mako da ya gabata a kauyen Jambali, da ke kusa da garin Bena.
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/HUEzyk9QvHZ6kSk4bH2U6K
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari