An tsinci gawar wata dalibar Jami'ar Najeriya yashe a gefen titi bayan ta bace ranar Laraba 17 ga watan Fabrairu.
Shafin ISYAKU.COM ya samo cewa yarinyar, yar shekara 26 a Duniya mai suna Fatima, ta bar gida da safiyar Laraba domin ta rubuta Jarabawa da za a yi karfe 8 na safe.
Sai dai tun wannan lokaci ba a sake jin duriyarta ba. An gano gawarta ne ranar 18 ga watan Fabrairu, a Gbagada U-Turn da ke karkashin gada a tagwayen hanyar Apapa-Oshodi a jihar Lagos.
Sai dai hukumomi a jihar Lagos basu ce uffan ba kawo yanzu dangane da mutuwar Fatima.
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/HUEzyk9QvHZ6kSk4bH2U6K
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari