A kalla dakarun sojin saman Najeriya 7 ne suka rasa rayukansu bayan rikitowar jirgin sama da suka hau wanda ya tunkari garin Minna da ke jihar Neja.Jaridar legit ta ruwaito.
An gano cewa an sanar da matsala a injin din jirgin wurin
10:39 na safe amma sai ya tarwatse a yayin da yake sauka a Abuja wurin karfe 10:48 na safe.
Jirgin saman ya tarwatse ne bayan da ya doke wata itaciyar mangwaro, ganau ba jiyau ba suka tabbatar da hakan.
Jaridar Daily Trust ta samu jerin sunayen sojojin da suka rasa rayukansau sakamakon faduwar jirgin saman.
Ga sunayen kamar haka:
1. Flt. Lt. Gazama
2. Flt. Lt. Piyo
3. Flg. Offr. Okpara
4. FS Olawumi
5. ACM Johnson
6. Sgt Oloka
Shugaban rundunar sojin saman Najeriya, Aire Vice Marshal Oladayo Amao ya bada umarnin binciken musabbabin wannan mummunan hatsarin.
https://chat.whatsapp.com/HUEzyk9QvHZ6kSk4bH2U6K
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari