An tsinci kwarangwam na kan mutum a unguwar Malala da ke garin Birnin kebbi babban Birnin jihar Kebbi ranar Talata.
Sai dai bayanai daga majiya mai tushe sun ce kwarangwam da aka samu na wata yarinya ce mai suna Wasila diyar Bala Mai tiles wacce ta bace kimanin wata daya da ta gabata a unguwar Malala.
Bayanai sun ce wani yaro mai bola jari ne ya gano wannan kwarangwam wanda aka lullube da gyale aka bizine.
Bayan da labarinya bulla, mahaifin yarinyar ya shaida gyalen diyarsa da ta bace tana sanye da shi.
Tuni dai jami'an tsaro suka fara bincike kan lamarin kamar yadda wata majiya ta shaida mana.
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/LKeYYgwzLbW8DdHbjNuEos
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari