An dauke wani basarake a Masarautar Zuru aka yi awon gaba da shi


Wasu mutane sun dauke wani basaraken garin Dega, rikon garin Tadurga, mai suna Dega Na'Allah, ranar Litinin 15 ga watan Fabrairu da misalin karfe 5 na yamma a karamar hukumar Zuru da ke Masarautar Zuru a kudancin jihar Kebbi.

Rahotanni sun ce ana zargin cewa wasu mutane dauke da makamai, sun tsayar da basaraken ne kuma suka saukar da shi daga babur da yake tukawa, lokacin da yake dauke da matarsa kan hanyarsa ta komawa gida, sun tsayar da shi a dai dai kofar barka da zuwa garin Ribah suka yi awon gaba da shi.

Tun ranar Litinin 15 ga watan Fabrairu, har zuwa yanzu, ba a ji duriyar inda yake ba tare da babur da yake tukawa.


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/HUEzyk9QvHZ6kSk4bH2U6K

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN