Almajirai 3 mutum 8 da matar aure sun kone kurmus a gobarar motar tankar man petur

Yara Almajirai guda uku tare da wasu mutum takwas sun kone kurmus har lahira, bayan wata mota tankar mai ta yi bindiga kuma ta kama da wuta a Gawu da ke babban Birnin tarayyar Najeriya Abuja, Jaridar Daily trust ta ruwaito.

Jaridar ta ce wadanda suka mutu a wannan ibtila'i sun hada da wata matar aure mai suna Halima Mohammed Yusuf, da shugaban kungiyar Banga ta Gawu, Adamu Ibrahim, da Dantala Usman, Umar Aliyu, Mohammed Hamza, Hassan Usman, Gambo Hamisu tare da Sani Abdulmutalib.

Wani ganau ba jiyau ba ya ce " Motar tankar mai ta fito daga gefen Lapai zuwa Izzom, amma garin kokarin kauce wa yin karo da Tileran motar Dangote saboda kokarin kauce wa rami, sai motar ta kwace wa Direba ta kauce kan titi ta je ta yi karo, sakamakon haka motar ta fadi man petur ya yi ta malala.

Ganin haka ya sa mutane suka je wajen da bokitai da jarkoki suka yi ta diban mai, ana cikin haka ne wata matar aure mai suna Halima ta je wajen, domin ta kori danta daga cikin masu diban mai, sai dài tsautsayi ya riga fata, domin dai kwatsam sai wuta ta tashi a wajen nàn take ta kone Halima da sauran jama'a da ke wajen.


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp 
https://chat.whatsapp.com/HUEzyk9QvHZ6kSk4bH2U6K

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu 
LATSA NAN 

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA 

Facebook.com/isyakulabari 


إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN