Wata mata a jihar Ondo ta sayar da jariri da ta haifa a kan kudi naira dubu dari kacal N100.000.
Matar mai suna Seun Oladayo mai shekara 22 a Duniya, ta sayar ma wani Pasto Jaririn ne jim kadan bayan ta haife shi. Daga bisani Pastor ya sanar da jami'an tsaro.
Matar yar asalin garin Abejoye ce da ke garin Ondo a karamar hukumar Ondo ta yamma.
Mun samo cewa wanda ya yi mata cikin ya rabu da ita ya gudu tun lokacin da ta shaida masa cewa tana da juna biyu.Ta ce tsananin wahala da kuncin rayuwa ya sa ta yanke shawarar sayar da Jaririn.
Yan sanda sun kama matar kuma auna gudanar da bincike.
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/LKeYYgwzLbW8DdHbjNuEos
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari