Tsohon mataimakin safeto janar na yan sanda ya rasu a jihar Sokoto


Rahoton jaridar  hausa.legit.ng sun nuna cewa Muhammad Tambari Yabo, mataimakin sufeto-janar na yan sanda mai ritaya, ya mutu.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa ya mutu a asibitin koyarwa na jami’ar Usman Danfodiyo, jihar Sokoto a ranar Asabar, 9 ga watan Janairu, bayan yar gajeriyar rashin lafiya.

Koda dai ba a bayyana musababbin ciwonsa ba, Legit.ng ta lura cewa babban jami’in dan sandan mai ritaya ya mutu ne a daidai lokacin da ake sake samun hauhawan wadanda suka mutu sakamakon annobar korona.

An gudanar da jana’izar marigayin da misalin karfe 2.30 na rana, a garin Yabo na Karamar Hukumar Yabo da ke Jihar Sokoto.

Gabanin ya kai mukamin Mataimakin Babban Sufeton ’Yan Sanda wato AIG, ya rike mukamin Kwamishinan ’Yan Sanda a Kaduna, Kano da Jihar Legas har sau biyu da kuma Oyo da Zamfara da Imo jaridar Aminiya ta ruwaito.



Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/J9zhUeQqg52KIxyFnYByJN

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN