Ganduje ya yi muhimmin zance kan zirga zirgan shanu daga arewa zuwa kudancin Najeriya


Shafin BBCHAUSA ta wallafa cewa Gwamnan jihar Kano da ke arewacin Najeriya Abdullahi Ganduje, ya ce ya kamata a samar da dokar da za ta haramta zirga-zirgar shanu daga arewa zuwa kudancin kasar.

Kafafen yada labarai na kasar sun ruwaito Ganduje na fadin haka a garin Daura da ke Jihar Katsina, lokacin da shi da sauran gwamnonin jam’iyyar APC suka je wurin shugaban kasar Muhammadu Buhari.

Ganduje ya ce matukar ba a dakatar da zirga-zirgar shanu tsakanin yankunan biyu ba, to ba za a taba kawo karshen rikicin manoma da fulani ba.

Gwamnan ya ce gwamnatinsa ta samar da wurin kiwo ga masu kiwo a wani daji da ke nusa da iyakar Kano da Katsina.

He said the settlement will have houses, a dam, an artificial insemination centre, and a veterinary clinic.

“Muna gina Ruga a dajin Samsosua da ke kan iyakarmu da Ktsina, kuma munyi nasara wajen shawo kan ‘yan fashin daji a yankin,” in ji Ganduje.


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/LKeYYgwzLbW8DdHbjNuEos

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN