Iklima Musa tana neman a karbar mata hakkinta daga wurin kishiyarta wacce ta watsa mata tafasasshen ruwa a jihar Filato, Linda Ikeji ta wallafa.
Idan za mu tuna, wacce ake zargi da aika-aikar mai suna Justina Peter ana nemanta ido rufe bayan lamarin da ya faru a Gindiri a karamar hukumar Mangu ta jihar Filato.
An gano cewa matar bata taba shiri da Iklima ba tun bayan da mijinta ya aurota a matsayin mata ta biyu a shekaru uku da suka gabata.
Kamar yadda Daily Trust ta bayyana, bayan kishiyoyin sun fara fada, mijinsu mai suna Ate Peter Manomi ya raba su.
Yayin da Iklima ta fito daga dakinta domin kwashe shanyarta, Justina ta watsa mata tafasasshen ruwan zafi.
Wannan harin ya bar Iklima da miyagun kuna a jikinta. Mijinsu Manomi, ya gaggauta mika Iklima asibiti kuma aka kwantar da ita.
"Na duka kasa in kwashe kayana da na wanke, ban san cewa ksihiyata ta taho ba da muguwar niyya. Ban taba tsammanin haka ba saboda an raba mu fadan.
"A lokacin da nake tashi tsaye, ta watsa min ruwa inda na fara ihu. Mijinmu ne ya fara zuwa. Inda nayi sa'a bai yi nisa ba. Da baya kusa da bamu san me zai faru ba." ta bayyana.
A wani labari na daban, 'yan sandan Najeriya sun sake damke mawallafin Sahara reporters, Omoyele Sowore a kan jagorantar wata zanga-zanga da yayi a babban birnin tarayya na Abuja.
Sowore tare da wasu 'yan gwagwarmaya sun shiga hannun 'yan sandan bayan da suka fito zanga-zanga mai suna #CrossoverWithProtest, zanga-zangar da suka shirya a dukkan fadin kasar nan ana gobe sabuwar shekara.
Wasu daga cikin masu zanga-zangar da suka arce ne suka tabbatarwa da Premium Times cewa an damke Sowore inda aka jefa shi daya daga cikin motocin 'yan sanda bakwai da aka tura wurin zanga-zangar.
Source: legit
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari