Bayan da wasu mutane dauke da makamai da ake zargin yan sa kai ne suka dauke Alhaji Mande Kanya da karfe 5 na yammacin ranar Lahadi 10/1/2021 a garin Kanya, da ke karamar hukumar Danko-Wasagu da ke Masarautar Zuru a kudancin jihar Kebbi, an sami gawarsa da safiyar Litinin 11/1/2021, ana zargin an sare kansa daga gangan jikinsa, bayan an kwakwale idanunsa yayinda aka daure hannayensa a bayansa, kuma aka barta a daji da ke wani kauye da ke kusa da garin Kanya.
Babu wani bayani kawo yanzu daga hukumomin tsaro na jihar Kebbi kan wannan lamari kafi lokacin rubuta wannan rahotu.
Sai dai wata majiya ta tabbatar mana cewa Gwamnatin jihar Kebbi ta bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan lamarin.
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari