Hukumar yaki da hana yaduwar cututtuka ta Najeriya (NCDC), ta bayyana cewa an samu karin mutane 712 da suka kamu da annobar korona a ranar Juma’a, 25 ga watan Disamba.
Hakan na kunshe ne a cikin sabbin alkaluman da hukumar ta wallafa a shafin Twitter. Ta kuma bayyana cewa karin mutane hudu sun mutu.
Sabbin mutanen da suka kamu sun fito ne daga jihohi 20 na kasar da suka hada da:
Legas: 388
Abuja: 77
Kwara: 39
Katsina: 35
Bauchi: 33
Plateau: 22
Ogun: 18
Akwa Ibom: 16
Delta: 13
Kaduna: 12
Osun: 12
Yobe: 11
Sokoto: 10
Kebbi: 8
Enugu: 6
Edo: 5
Ondo: 3
Niger: 2
Kano: 1
Oyo: 1
Gaba daya jimlar mutane 82747 ne suka harbu da cutar a Najeriya, yayin da 1,246 suka mutu sannan a yanzu an sallami mutane 70,239 bayan sun warke.
A wani labari, an yi ma yarima mai jiran gado na kasar saudiyya, wanda shine ministan tsaron kasar, Mohammad bin Salman, allurar cutar Korona ranar Juma'a, 25 ga watan Disamba, 2020.
Bayan da Yarima ya karbi nasa, ministan al'adan kasar, Yarima Badr Farhan, ya karbi nashi rigakafin.
Ministan lafiyan kasar, Dakta Tawfiq Al-Rabiah, ya godewa yariman bisa mulkin da ya nuna wajen samarwa al'ummar kasar rigakafin.
Source: legit
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari