Rahotanni daga jihar Borno sun ce yan Boko Haram sun sace mutum 35 matafiya a kan hanyar Damaturu zuwa Maiduguri da yammacin ranar Juma'a.
Rahotan TVC NEWS ya ce yan Boko Haram sun farmaki ayarin motocin matafiya ne kusa da garin Garin-Kuturu Jakana da misalin karfe 4 na yamma.
Rahotun ya kara da cewa maharan sun zo ne da motci kirar Hilux guda biyar, sanye da tufafin soji, suka kafa shinge kamar suna duba ababen hawa, daga bisani suka kaddamar da farmakinsu kan matafiya, kuma suka kone wasu motoci kafin su tafi.
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari