Mai ba Gwamnan jihar Kano shawara kan harkokin addini Ali Muhammed Alibaba ya nemi gafarar tsohon Gwamnan jihar Kano Engr Rabiu Musa Kwankwaso.
DailyNigerian ta ruwaito cewa Alibaba ya fada tsaka mai wuya ne bayan yan sandan jihar Kano sun kama shi tare da yi masa tambayoyi bayan Manajan Kampanin man Aliko Oil a Company Ltd ya shigar da kararsa wajen yan sanda a Bompai ranar Alhamis.
Alibaba ya yi zargi a wani shirin radio cewa Kampanin man mallakan Kwankwaso ne. Ya kuma kalubalanci Kwankwaso cewa ya rantse idan Kampanin man ba nashi bane.
Ya Kara da cewa kalar fari da ja na Kampanin man ya yi kama da kalar da Kwankwaso ke amfani da shi a siyasarsa.
Bayan yan sanda sun yi masa tambayoyi na tsawon awanni. An yi zargin cewa yansanda sun garkame shi, daga bisani suka bayar da shi beli, da yarjejeniyar cewa zai koma gidan rediyo da ya yi wannan zargi domin ya janye ikirarinsa.
Ranar Asabar Alibaba ya bayyana a shirin gidan rediyo kuma ya janye ikirarinsa tare da ban hakuri ga Kampanin mai na Aliko, da kuma Rabiu Musa Kwankwaso.
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari