Gwamnatin Najeriya ta bayar da umarnin rufe makarantu da wuraren shaƙatawa


Kwamitin shugaban ƙasa da ke yaƙi da annobar korona, ya sake bayar da umarni ga ma'aikatan gwamnati daga mataki na 12 zuwa ƙasa da su zauna a gida har nan da makonni biyar.

A cewar kwamitin wanda ke ƙarƙashin jagorancin sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha, duka makarantu a faɗin ƙasar za su zama a rufe har zuwa watan Janairun 2021.

Kwamitin ya bayyana cewa gidajen rawa da wuraren shan barasa da kuma wuraren motsa jiki za su ci gaba da zama a rufe a ƙasar.

Kwamitin ya bayar da umarnin rufe gidajen abinci

Haka kuma gwamnatin ta saka takunkumi kan taruka irin na addini inda kwamitin ya ce ko wane wuri kada ya ɗauki sama da kashi 50 cikin 100 na mutanen da yake ɗauka a baya.

Gwamnatin ta kayyade tarukan addini su zama kasa da kashi 50 na inda wuraren ibada ke ɗauka, domin tabbatar da ba da tazara da kuma sanya takunkumi.

Boss Mustapa ya ce dukkan taron da za a yi ya wuce mutum 50 to a tabbatar da an yi shi a buɗaɗɗen waje mai makon a ɗakin taro.

Haka na ababan hawa su ɗauki kashi 50 na fasinjan da suke iya ɗauka domin bin dokar ba da tazara.

Source: BBCHausa


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/J9zhUeQqg52KIxyFnYByJN

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN