Yan sandan jihar Ondo a kudancin tarayyar Najeriya, sun kama wasu mutum uku bisa zargin kashe mutane ta hanyar yi masu yankan rago a wani gida a garin Igbokoda, da ke karamar hukumar Ilaje a jihar ta Ondo.
Wadanda yan sanda suka kama su ne Bode Omoboye, Eric Ogungbamila da Tayo Loto wanda ake zargi da kasancewa mai yi masu leken asiri.
Sanarwar yansanda ya nuna cewa ana tsare da mutanen a ofishin yansanda na Igbokoda yayin da ake ci gaba da bincike.
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari