Matasa a garin Daudu da ke karamar hukumar Goma a jihar Benue, sun gudanar da zanga zangar lumana ranar Lahadi 1 ga watan Satumba bisa zargin karuwar bacewar Mazakutar maza a garin.
Matasan sun yi zargin cewa mutum 7 ne suka rasa Mazakutarsu a wani yanayi mai ban mamaki a garin.
Zanga zangar ta faro ne daga Kasuwar Daudu har zuwa babban hanyar mota ta Makurdi zuwa Lafia, yanayi da ya haifar da cinkoson ababen hawa da dama a hanyar kafin yansanda suka je suka tarwatsa matasan.
Kazalika rahotu ya ce wani matashi ya kashe kansa ranar 11 ga watan Oktoba bayan an zarge shi da sace Mazakutar wani matashi a garin.
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari