Yan sanda sun kashe mutane biyu a Kano, duba dalili


An shiga halin fargaba a jihar Kano bayan kisan wasu mutane biyu da ake zargin yan sandan da ke yaki da yan daba a jihar da aikatawa.

Yayinda ba a fitar da kowani jawabi da ke tabbatar da hakan daga mahukunta ba, an tattaro cewa an harbe matasan ne a unguwar Sharada lokacin da sashin yaki da yan daba suka ziyarci yankin.

Wani rahoto da ba a tabbatar ba ya nuna cewa yan sandan kan matsa wa matasa a yankin amma sai aka samu tirjiya a wannan rana ta Asabar wanda ya yi sanadiyar bude wuta da mutuwar mutum biyu.

Matasan da aka kashe sune Abubakar Isah da Ibrahim Sulaiman (Mainasara) jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Rundunar yan sandan jihar Kano bata riga ta yi martani a kan lamarin ba yayinda aka tattaro cewa an birne mutanen da aka kashe a ranar Lahadi.

A wani labarin, wani abun al'ajabi ya afku a birnin Makurdi,jihar Benue inda wani mutum mai matsaikatan shekaru ya cinnawa kansa da budurwarsa wuta.

Bayanai sun nuna cewa mutumin wanda har zuwa lokacin tattara wannan rahoton ba'a kai da gano kowaye ba, ya siyo fetur, ya kulle kansa a ɗaki tare da buduruwarsa a ciki kafin ya banka musu wuta gabaki ɗayansu.

Source: Legit


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/J9zhUeQqg52KIxyFnYByJN

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN