Hukumar zaɓen Ghana ta ce 'yan sanda da sojoji da 'yan jarida da direbobin motar ɗaukar marsa lafiya ba za su jefa ƙuri'a ba a zaɓen ranar 7 ga watan Disamba mai zuwa.
Hukumar Ghana Electoral Commission (GEC) ta ce waɗannan rukunin mutanen da ta lissafa na cikin masu kaɗa ƙuri'a na musamman da za su yi zaɓen tun 1 ga Disamba.
Tuni GEC ta wallafa sunayen waɗanda za su jefa ƙuri'ar a rana ta musamman ga mutanen da ke aiki na musamman, waɗanda kaɗa ƙuri'ar ka iya shafar aikinsu a ranar zaɓe.
Mutanen sun haɗa da 'yan sanda da sojoji da masu tuƙa motocin ɗaukar marasa lafiya da 'yan jarida da sauransu.
Sai dai hukumar ta gargaɗi waɗanda suka yi rajistar zaɓe na musamman cewa idan suka gaza kaɗa ƙuri'a ranar 1 ga wata to ba za su yi zaɓen ba ranar 7.
"Wajibi ne masu zaɓen su tabbatar cewa sun bi matakan da suka dace domin tantance bayanansu saboda gudun kar a haramta musu kaɗa ƙuri'a tun da GEC ba za ta bari su yi zaɓe ba ranar 7 ga wata," in ji hukumar.
Source: BBC
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari