Shugaban jami'an tsaron farin kaya na NSCDC na Najeriya Mr. Abdullahi Gana, ya yi allah wadai da matakin famakin jami'an VIO da wasu daga cikin jami'an NSCDC suka yi a kan hanyar Abuja zuwa Keffi.
Jami'an VIO na gudanar da akin kula da ababen hawa a kan hanyar lokacin da jami'an NSCDC suka isa wajen cikin wata babban Bas da ke dauke da jami'an kan hanyarsu ta komawa gida. Rahotanni sun ce an sami yar damuwa tsakanin jami'an VIO da na NSCDC wanda ya kai ga jami'an NSCDC suka ci zarafin jami'an VIO.
NAN ta labarta cewa Kakakin NSCDC na kasa Mr Kalu Okeh, ya ce hukumar NSCDC za ta hukunta jami'anta da ke da hannu a wannan aika aika.
Ya kuma ce hukumar ta jaye motar Bas da ke daukan jami'anta zuwa Keffi wajen zuwa da komawa gida idan an tashi daga ofis sakamakon wannan matsala
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari