Fusatattun matasa sun banka ma wani da ake zargi barawo ne wuta bayan sun kashe shi a garin Idjerhe da ke karamar hukumar Ethiope ta kudu a jihar Delta ranar Talata 24 ga watan Nuwamba.
ISYAKU.COM ya samo cewa wanda aka kama yana daya daga cikin gungu 2 na masu aikatab laifi da ke addabar mutane a yankin. Ya bi wata yarinya ya razanata da bindigar roba ya karbe waya da kudade da ke hannunta.
Rahotanni sun ce bayan yarinyar ta kula cewa bindigar roba ne, sai ta yi kururuwa har matasa suka nufo wajen, sakamakon haka barawon ya ruga da gudu kuma jama'a suka biyo shi har suka kama shi suka yi masa duka har ya mutu, daga bisani suka banka wa gawarsa wuta.
Kakakin hukumar yansandan jihar DSP Onome Onovwakpoyeya ya tabbatar da aukuwan lamarin.
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari