Wata babban Kotun Bisho da ke gabacin kasar Afrika ta kudu ta daure wani kasurgumin mai fyade dan shekara 44 a Duniya Malibongwe Ncokolo rai da rai har sau 7, da shekara 300 a Kurkuku bayan ta kama shi da laifin yi wa mata da yan mata fyade.
Ranar Juma'a 6 ga watan Nuwamba Kotun ta daure Ncokolo wanda kamunsa ranar 7 ga watan Yuni 2017 ya jawo fallasa da kawo karshen mumunan tashin hankali da mata da yan mata ke fuskanta na fyade a Mdantsane a Afrika ta kudu.
Ncokolo ya yi ta cin zarafin mata da yan mata da keta, ta hanyar fyade da gayya tun 2014 kafin dubunsa ta cika a 2017 lokacin da ya yi kokarin yi wa wata yarinya fyade amma ta kubuta kuma ta nemi taimakon jama'a.
Shaidu 140 ne tare da mata 22 da ya ci zarafinsu ta hanyar fyade suka bayyana a Kotu domin bayar da shaida.
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari