Jihar Kwara za ta dena biyan tsaffin gwamnoni da mataimakansu fansho


Gwamnatin Jihar Kwara zata soke dokar biyan tsaffin gwamnoni da mataimakansu kudaden fansho kamar yadda gwamnan jihar ya sanar a shafinsa na Twitter. Wannan matakin ya yi kama da wadda gwamnatin Jihar Legas ta dauka a baya bayan nan inda ta ce za ta dena biyan tsaffin gwamnonin da mataimakansu kudaden fansho.

Gwamna Abdulrazak yace jihar na bukatar kudade don inganta rayuwar al'ummar jihar, inda ya ce ya yi imanin zai fi dacewa ayi amfani da kudaden jihar wurin magance talauci da samar wa matasa ayyukan yi.

A bangarenta, gwamnatin na Legas ta ce ta dauki matakin ne don rage kudaden da gwamnatin jihar ke kashewa a kansu don ta mayar da hankali kan yin ayyukan da zasu inganta rayuwar 'yan jihar.

Tsohon gwamnan jihar Legas kuma jagoran jam'iyyar APC na kasa, Ahmed Bola Tinubu a martanin da ya yi ya ce yana goyon bayan matakin da gwamnatin na Legas karkashin jagorancin Gwamna Babajide Sanwo-Olu ta dauka. Ya ce zai koma jam'iyya mai mulki ta APC yana mai ikirarin cewa APC zata bawa dan yankin sa na kudu maso gabas takara a zaben 2023.

Source: Legit



Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/J9zhUeQqg52KIxyFnYByJN

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN