Mutum shida sun mutu sakamakon mumunar hadarin mota da ya auku tsakanin tankar man petur da wata motar fasinja a garin Nkwelle Ezunaka wanda ke kan hanyar Enugu zuwa Onitsha ranar Lahadi 22 ga watan Nuwamba.
Fiye da mutum 11 da suka sami raunuka an garzaya zuwa Asibitin Iya-Enu Mission Hospital domin samun kulawan Likitoci.
Bayan tabbatar da aukuwan lamarin, Kakakin hukumar kiyaye hadaurra ta kasa FRSC reshen jihar Anambra Nkwelle Ezunaka, ya ce mutum 17 hatsarin ya rutsa da su.Ya ce 11 daga cikin adadadin maza ne, yayin da ragowar adadadin kuwa mata ne.
Ya ce an adana gawakin wadanda suka mutu a Motuware. Sai dai ya alakanta hatsarin da mugun gudu da direbobi suka yi.
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari