Wani matashi mai shekara 27 mai suna Prince Mieyebi ya rasa ransa bayan wasu mutane uku sun kashe shi ta hanyar caka masa wuka bayan ya ci Naira Miliyan goma sha biyar N15m a wasar Nijabet a birnin Warri na jihar Delta.
Bayanai sun nuna cewa an kashe saurayin ne lokacin da yake kulle shagonsa a kasuwar Ogbe-Ijoh da ke karamar hukumar Warri ta kudu ranar 27 ga watan Nuwamba.
Wadanda suka caka masa wuka a wurare da dama a jikinsa sun tsere da wayar salularsa.Ya mutu kafin a kaishi Asibiti.
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari