An kashe Malamin Mujami'a da aka zarge shi da sace Mazakutar matasa a garin Daudu na jihar Benue.
Hadimin Gwamnan Benue kan harkar labarai Olikita Ekani ya ce an kashe Pastor Uhembe Jacob kuma a ka bizine gawarsa a wani kabari mara zurfi.
Yayin da ya sako hotunan Pasto Ehembe, Ekani ya ruwaito cewa "Babban la'ana a garin Daudu"
"Wannan shi ne Pastot Uhembe Jacob wanda aka yi wa kazafin sace Mazakutar jama'a a garin Daudu"
"Bayan sun kone duk gidajensa, Mujami'arsa, tare da duk abin da ya mallaka, daga karshe sun sace shi suka tafi da shi daji suka kashe shi a kan lamari da bai san komi ba akai, kuma suka bizine shi a kabari da babu zurfi.
" Laifinsa kwaya daya ne kadai tilau...domin yana samun ci gaba cikin gaggawa!" inji Ekani.
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari