Ana rikici yanzu haka tsakanin Hausawa da Yarabawa a Fagba, Iju-Ishaga, karamar hukumar Ifako-Ijaye inda aka kona gidajen mutane kuma hankulan mazauna sun tashi, cewar Vanguard. Har yanzu babu jami'an tsaron da suka je kuma ba'a adadin wadanda abin ya shafa ba tukun.
Kakakin hukumar yan sanda jihar, ya tabbatar da hakan kuma ya yi kira ga shugabannin garin su yiwa matasans magana. Ya ce ita kanta hukumar yan sandan na fuskantar matsala. "Akwai dokar hana fita kuma kowa ya koma gida. Aiki ya yiwa yan sanda yawa, mu hada kai domin kawo karshen lamarin," Kakakin yace. Daya daga mazauna yankin, Aina, ya bayyanawa The Punch cewa "Mun kasa fita daga gudajenmu.
Tun ranar Talata suka fara fada. Mun yi tunanin abin ya tsaya jiya ne amma suka cigaba yau." "Ban san abinda ya janyo fadan ba, kawai na ga mutane na ta guje-guje." A bangare guda, mai bada shawara na musamman ga shugaban kasa kan kafar watsa labarai, Femi Adesina ya ce wasu masallatai da coci-coci da wasu kafafen baza labarai na kiyayya. Ya kara da cewa zanga zangar EndSARS wata dama ce da wasu suke amfani da ita don watsa sakonnin kiyayya kamar yadda The Punch ta ruwaito.
Source: Legit
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari