Shugaba Muhammadu Buhari ya zabi wadanda yake son a nada sabbin shugabannin hukumar lura da wutar lantarki a Najeriya watau NERC.
Shugaban kasar ya aike da sunayensu majalisar dokokin tarayya domin tabbatar da su.
Shugaban majalisar dattawa, Ahmed Ibrahim Lawan, ya karanta wasikar da Buhari ya aiko musu a zauren majalisa ranar Talata, 20 ga watan Oktoba, 2020.
Wadanda Buhari ya zaba sune:
1 . Engr. Sanusi Garba - Shugaba
2. Musiliu Olalekan Oseni - Mataimakin shugaba
3. Aisha Mahmud - Kwamishana
A bangare guda, majalisar dattawa, a ranar Talata ta yi kira ga Shugaba Muhammadu Buhari ya yi wa 'yan Najeriya jawabi nan take a kan zanga-zangar da matasa ke yi a jihohin kasar game da cin zali da 'yan sanda ke yi da kuma neman kawo gyara a gwamnati.
Majalisar ta kuma bukaci jami'an 'yan sanda su bawa matasa da ke zanga-zangar ta EndSARS kariya daga 'yan daba da ke neman mamaye zanga-zangar kamar yadda The Punch ta ruwaito.
Source: Legit
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari