Wasu da ake zargin matsafa ne sun kashe wani mai gadi dan shekar 43 kuma suka gundule kansa a cikin al'umman Oka-Akoko shelkwatar karamar hukumar Akoko ta yamma a jihar Ondo.
Wanda aka kashe mai suna Rotimi Olukoju, yana aiki da wani Banki ne kafin mutuwarsa tranar Alhamis 29 ga watan Oktoba da yamma bayan an uar da gawarsa a gefen hanya a cikin daji.
Wasu kauyawa sun ce an kashe Olokoju a kan hanyarshi ce ta zuwa gona a yankin Iwaro da ke Oko-Akoko, kuma aka cire wasu sassan jikinsa.
Wani dagacikin zuri'ar mamacin ya tabbatar da faruwar lamarin ranar Juma'a, ya ce yan sanda su kai gawar Olukoju dakin ajiye gawa.
Ya ce mamain ya fara aiki an Bankin ne domin ya sami abin rufa wa iyalinsa asiri kafin ya sami ajalinsa a hannun matsafa.
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari