Mutum 3 sun tone kabari 10 suka datse kawunan mamata domin tsafi


Yansanda sun gurfanar da wasu uku a gaban Kotun Maajistare a Ado-Ekiti bisa zargin hakar Kabari suka tone gawakin 10 da aka binne kuma suka yanke kawunasu bisa dalilan tsafi.

Wadanda aka kama su ne Kola Fatoye mai shekara 40, da Abimbola Fatoyedan shekara 35, da Ahmed Ojo, shekara 56 a Duniya.

Mai gabatar da kara ta yansanda Monica Ikebuilo ta gaya wa Kotu cewa wadanda ake zargi sun aikata laifin ne tun watan Maris zuwa Satumba a garin Prun-Ekiti.

Ikebuilo ta ce gawakin da mutanen suka tone na Philip Akintayo, Moreani Ajayi da wasu mutun takwas ne., kuma sun yi hakan ne bisa dalilan tsafi, kamar yadda ta gaya wa Kotu.



Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JKBP5KgalYg3iQRBQoFVAE

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/L4xvcwRGM496Eep5J53zXt

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN