Tsohon gwamnan jihar Kano Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya buɗe sabon gidan rediyo a jihar Kanoda ke arewacin Najeriya.
Gidan rediyon mai suna Nasara FM zai fara watsa shirye-shiryensa na gwaji a kan mita 98.5 a zangon FM daga ranar Alhamis, ta hanyar sanya karatun alkur'ani mai girma.
Shugaban gidan rediyon Maude Rabiu Gwadabe wanda tsohon ma'aikacin BBC ne, ya ce suna fatan samun karɓuwa a wajen al'ummar jihar.
Gidan rediyon ya samu amincewar hukumar kula da kafafen watsa labarai ta Najeriya wato NBC.
Source: BBC
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari