Rahotanni sun ce matar mai suna Blessing, ta haifi Jariri ne bayan an yi mata tiyata a Asibitin Mojo Hospitals da ke Egbeda Shasha a birnin Lagos. Kuma Asibitin ta caji Blessing Naira dubu dari uku da hamsin N350,000, amma daga bisani Daraktar ayyukan jinya na Asibitin ya rage mata kudin zuwa Naira dubu dari biyu da hamsin, N250,000.
Blessing ta biya Naira dubu dari da sittin, amma ta kasa biyan sauran cikon kudi Naira dubu casa'in N160,000. Sakamakon haka, Asibitin ta ki ta sallami Blessing har tsawon wata bakwai bayan ta haihu.
Sai dai majiyarmu ta ce mijin Blessing Makanike ne, kuma baya da hanzarin biyan wannan kudi, sakamkon haka suke kira ga jama'a su taimaka masu da cikon kudin N90,000 domin a sallami matarsa daga Asibitin.
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/