Yan kwanaki bayan kaddamar da Godwin Obaseki a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan Edo, shugabar kotun daukaka kara, Justis Monica Dongban-Menem ta kafa kotun sauraron karar zabe domin duba kararrakin da zai fito daga zaben.
A cewar jaridar The Nation, an tsara zaman sauraron kararrakin zaben a harabar babbar kotun da ke Benin, babbar birnin jihar Edo. Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da sakataren kotun zaben, Sunday Martins ya fitar a ranar Talata, 22 ga watan Satumba.
“Ana sanar da jama’a cewa mai girma shugabar kotun daukaka kara ta Najeriya, Justis M. B Dongban Mensem ta kafa kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan da aka gudanar a jihar Edo.” Jawabin ya ci gaba da bayyana cewa shugaban alkalai na jihar Edo, Justis Edigin ya amince da amfani da dakin sauraron kararrakin zabe da ke harabar babbar kotu a Sapele Road, birnin Benin don sauraron korafe-korafen.
Legit.ng ta tuna cewa Obaseki na PDP ya kayar da Ize-Iyamu na APC a zaben. Sai dai Ize-Iyamu wanda yace har yanzu yana nazarin sakamakon zaben ne bai bayyana ko zai kalubalanci sakamakon ba a kotu.Da wannan shahadar, Obaseki da Shaibu sun cika sharrudan dokar zabe domin rantsar da su ranar 12 ga Nuwamba, 2020 a Benin City domin wa'adinsu na biyu a ofis.
Source: Legit
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/