Kwamitin zartarwa na jam'iyar APC a jihar Ekiti, ta dakatar da Gwamna Kayode Fayemi daga jam'iyar.
A wata sanarwa da jam'iyar APC ta fitar ranar Juma'a 25 ga watan Satumba, ta yi zargin cewa ta dakatar da Gwamnan ne sakamakon " Ayyukan cin amanar jam'iyar musamman irin rawa da ya taka lokacin zaben Gwamnan jihar Edo da aka kammala kwanan nan".
Haka zalika takardar ta yi zargin cewa "Kwanaki biyar kafin zaben jihar Edo, Gwamna Fayemi ya ba wani jigo a jam'iyar PDP, Femi Kayode masauki a fadar Gwamnatin jihar Ekiti, da ke Ado Ekiti, kuma suka kitsa yadda za a gudanar da Juyin mulki akan jam'iyar APC a jihar Edo.
Gwamna Fayemi ya kuma taka rawa wajen ganin jam'liyar APC ta sha kasa a zaben Gwamnan jihar Oyo". Kamar yadda takardar ta sanar.
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/