Yanzu yanzu: Gwamnan jihar Sokoto Aminu Tambuwal ya dakatar da hukumar Hisbah na jihar

 


Gwamnan  jihar Sokoto  Aminu Tambuwal, ya dakatar da hukumar Hisbah na jihar bisa zargin "Rarrabuwa"

Daily Trust ta labarta cewa ba wannan ne karo na farko da aka dakatar da hukumar ba,. Idan ba ku manata ba, Kwamishinan harkokin addini na jihar Sokoto, Mani Maishinku Katami, ya sanar da dakatar da hukumar Hisbah na jihar Sokoto shekara uku da suka gabata, kafin daga bisani aka dage dakatarwar.


A wata sanarwa da ta fito daga Hadimin Gwamna kan harkar watsa labarai Muhammad Bello, ya ce an kafa Kwamitin mutum 36 domin daidaita  ayyukan hukumar tare da samar da shawara kan ka'idan yadda Hisbah ya kamata ta gudanar da ayyukanta bisa tsarin doka da ta kafa ta.


An nada Wazirin Sokoto, Farfesa Sambo Wali Junaidu a matsayin shugaban Kwamitin, yayin da Sakataren din-din-dim a ofishin Kabinet  Alhaji Bande Rikina ya zama Sakataren kwamitin.



Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JKBP5KgalYg3iQRBQoFVAE

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/L4xvcwRGM496Eep5J53zXt

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN