Gwamnan jihar Sokoto Aminu Tambuwal, ya dakatar da hukumar Hisbah na jihar bisa zargin "Rarrabuwa"
Daily Trust ta labarta cewa ba wannan ne karo na farko da aka dakatar da hukumar ba,. Idan ba ku manata ba, Kwamishinan harkokin addini na jihar Sokoto, Mani Maishinku Katami, ya sanar da dakatar da hukumar Hisbah na jihar Sokoto shekara uku da suka gabata, kafin daga bisani aka dage dakatarwar.
A wata sanarwa da ta fito daga Hadimin Gwamna kan harkar watsa labarai Muhammad Bello, ya ce an kafa Kwamitin mutum 36 domin daidaita ayyukan hukumar tare da samar da shawara kan ka'idan yadda Hisbah ya kamata ta gudanar da ayyukanta bisa tsarin doka da ta kafa ta.
An nada Wazirin Sokoto, Farfesa Sambo
Wali Junaidu a matsayin shugaban Kwamitin, yayin da Sakataren din-din-dim a ofishin Kabinet Alhaji Bande Rikina ya zama Sakataren kwamitin.
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/