Jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) mai mulki a jihar Adamawa na iya fuskantar kalubale wajen zarcewa a jihar a 2023 idan har shirin siyasa da shugabannin All Progressives Congress (APC) ke yi ya cimma nasara. Legit.ng ta runa cewa APC ta rasa jihar a 2019 sakamakon wani rikici da aka kasa sasantawa tsakanin tsohon gwamnan jihar, ibrilla Bindow, da wasu shugabannin jam’iyyar.
Jaridar The Nation ta ruwaito cewa wasu yan asalin jihar da ake ganin mutuncinsu na aiki don hanin sun kwato jihar a zabe na gaba. Wadannan mutane kuwa sune babban sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha da tsohon SSG, David Babachir. An tattaro cewa Nuhu Ribadu, tsohon shugaban hukumar EFCC, tsohon gwamna Bindow, da surukin shugaban kasa Muhammadu Buhari, Ahmed Halilu (Mudi), na aiki sosai don dawo da APC a jihar.
Rahoton ya kuma bayyana cewa “Sanata mai wakiltan yankin Adamawa ta tsakiya a majalisar dokokin tarayya, wani mamba mai wakiltan Jada/Ganye/Mayo-Belwa/Toungo a majalisar wakilai, Abdulrazak Namdas, da tsohon mataimakin gwamnan jihar, Babale Martins” na cikin shirin jam’iyyar na kwato jihar a 2023.
Tsohon gwamnan jihar Bindow ya sha kaye a hannun dan takarar jam’iyyar PDP, Ahmadu Fintiri a zaben 2019. A wani labarin kuma, mun ji cewa tsohon gwamnan jihar Adamawa, Bala James Ngilari, ya sauya sheka zuwa jam’iyyar All Progressives Congress (APC). Da yake bayar da dalilansa na sauya sheka,
Ngilari ya yi korafin cewa jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) a jihar ba ta yi masa adalci. Ya ce bada dadewa ba za a fitar da jawabin sauya shekarsa, inda ya kara da cewa wasu jiga-jigan PDP da dubban magoya bayansu za su same shi a APC.
Source: Legit
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/