An kama wani Jami’in Lafiya da yayi barazanar kashe shugaba Buhari

Wani jami’in lafiya da aikin sanin makamar aiki da hukumar NAFDAC, Solomon Akuma ya shuga hannun jami’an ‘yansandan Najeriya bisa zargin furta cewa zai sa a kashe shugaban kasa, Muhammadu Buhari da Abba Kyari.

Wanine ya tambayeshi shin idan ya samu Dala Miliyan 1 me zai fara tunanin yi? Sai ya mayar da martani ta shafinsa na Twitter cewa abu na farko da zai yi shine zai dauko hayar gwanin harbi daga kasar Rasha ya kashe masa shugaba Buhari da tsohon shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Marigayi Abba Kyari.

An tsare akuma tsawon watanni 3 ba tare da gurfanar dashi a gaban kotu ba inda daga baya kuma aka kaishi kotu ana zarginshi da laifukan ta’addanci da yiwa gwamnati bore da barazana ga shugaban kasa, Muhammadu Buhari

Sahara Reporters ta ruwaito cewa zuwa yanzu ya kwashe kwanaki 150 a daure kuma kotu ta hana belinsa inda aka saka ranar 7 ga watan October a matsayin Ranar ci gana da sauraren karar.

hutudole


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JKBP5KgalYg3iQRBQoFVAE

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/L4xvcwRGM496Eep5J53zXt

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN