Hukumar yan sanda a jihar Anambara ta ce an kaddamar da bincike domin gano gaskiyar lamari gaba da kisan Bokan da ake zargi wani Fasto da shi. A wani takardar da aka saki ranar Juma'a a Awka, babbar birnin jihar Anambara, kakakin hukumar yan sandan jihar, Haruna Mohammed, ya ce Bokan da aka kashe, Oliver Ugwu, na da shekaru 60 a duniya kuma mazaunin kauyen Umusiome ne a Nkpor, kusa da Onitsha.
Ya ce Faston, Uchenna Chukwuma, wanda mazaunin titin Ugwuezue ne a unguwar ya kashe Bokan ta hanyar sara da adda ranar 3 ga Satumba, 2020. "Mai laifin, wanda asalin dan garin Amagunze ne a karamar hukumar Nkanu ta gabas ya bayyanawa yan sanda yayin bincike cewa Ubangijinsa ne ya umurceshi ya kashe bokan," Kakakin yan sanda ya bayyana.
"Ya kara da cewa Bokan na damunsa a ruhance kuma ya hana shi samun nasara a rayuwa da arziki a duniya." Haruna yace jami'an yan sandan dake ofishin Ogidi karkashin DPO Ekuri Remiguis sun ziyarci idan abin ya faru kuma suka garzaya da bokan asibitin Iyi Enu. Ya ce yayinda aka isa asibitin Likita ya tabbatar da cewa ya mutu kuma aka ajiye gawarsa a dakin ajiye gawawwaki domin bincike.
Source: Legit
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/ JKBP5KgalYg3iQRBQoFVAE
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/ L4xvcwRGM496Eep5J53zXt
Ya ce Faston, Uchenna Chukwuma, wanda mazaunin titin Ugwuezue ne a unguwar ya kashe Bokan ta hanyar sara da adda ranar 3 ga Satumba, 2020. "Mai laifin, wanda asalin dan garin Amagunze ne a karamar hukumar Nkanu ta gabas ya bayyanawa yan sanda yayin bincike cewa Ubangijinsa ne ya umurceshi ya kashe bokan," Kakakin yan sanda ya bayyana.
"Ya kara da cewa Bokan na damunsa a ruhance kuma ya hana shi samun nasara a rayuwa da arziki a duniya." Haruna yace jami'an yan sandan dake ofishin Ogidi karkashin DPO Ekuri Remiguis sun ziyarci idan abin ya faru kuma suka garzaya da bokan asibitin Iyi Enu. Ya ce yayinda aka isa asibitin Likita ya tabbatar da cewa ya mutu kuma aka ajiye gawarsa a dakin ajiye gawawwaki domin bincike.
Source: Legit
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/