Jaridar Daily Trust ta gano cewa, lamarin ya faru ne bayan cunkoson kan titin na ranar Lahadi tare da ruwa mai karfi da aka yi na sama ya kawo fadawar wani katon rami Babu wanda ya rasa ransa a yayin da lamarin ya faru, ganau ba jiyau ba ya sanar da hakan.
A ranar Litinin, an gano cewa hanya daya ce ke aiki inda jami'an tsaro suka garkame dayar. Jami'an kiyaye hadurran kan titi na tarayya (FRSC) ne suke bai wa masu ababen hawa hannu don sauya hanya.
Wani dan achaba mai suna Suleiman Umar, wanda ya zanta da manema labarai, ya ce an sanar da shi cewa ramin ya rufta bayan da wasu manyan motocin siminti biyu suka wuce ta kan gadar.Masu achaba kuwa sun ci gaba da amfani da hanyar da ramin yake amma ta gefen da abun bai shafa.
Source: Legit
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Domin samun sassauka, ingattacciya kuma kwakkwarar DATA ta MTN, latsa nan https://chat.whatsapp.com/